1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Guinea-Bissau ba za ta mika Bozize ba

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 8, 2024

Shugaba Umaro Sissoco Embalo na Guinea-Bissau ya ce ba zai mika tsohon shugaban kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya Francois Bozize da ke fuskantar sammacin kasa da kasa ba.

https://p.dw.com/p/4fe6s
Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya | Tsohon Hambararren Shugaban Kasa | Francois Bozize
Tsohon hambararren shugaban kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya Francois BozizeHoto: Florent Vergenes/AFP

Wata babbar kotu ta musamman da ke samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya a Bangui babban birnin kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiyar ce dai, ta sanar da sammacin kame Francois Bozize a wani mataki na tuhumar da ake masa kan laifukan cin zarafin dan Adam da masu gadinsa lokacin yana shugaban kasa suka aikata tsakanin shekara ta 2009 zuwa 2013 a kurkukun fararen hula da kuma sansanin bai wa sojoji horo. Mai shekaru 77 a duniya, Bozize ya karbe mulkin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a shekara ta 2003 a wani juyin mulki da ya yi, kafin shi ma a kifar da gwamnatinsa bayan shekaru 10. A yanzu dai Bozize na jagorantar babbar kungiyar tawayen kasar, kuma tun a shekara ta 2023 yake neman mafaka a Guinea-Bissau din da Shugaba Umaro Sissoco Embalo ke muka.