1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta nemi Turai ta tsare kanta

Yusuf Bala Nayaya
August 27, 2018

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya bayyana a ranar Litinin cewa zai gabatar wa Kungiyar Tarayyar Turai bukatar kara inganta tsaronta, ta yadda kasashen kungiyar za su yi watsi da dogara da Amirka.

https://p.dw.com/p/33rev
Emmanuel Macron  Rede Paris Frankreich
Hoto: picture-alliance/dpa/G. Gorges

A cewar Shugaba Macron bukatar tasa za ta zo baro-baro nan gaba "cikin watanni masu zuwa". Macron ya bayyana haka ne ga jami'an diflomasiya 250 da 'yan majalisa da kwararrun masana tsakanin kasa da kasa da suka hadu bayan dawowa daga hutun bazara.

Wannan bayanan na Shugaba Macron na zuwa ne yayin da kalaman Shugaba Donald Trump ke nunar da yadda shugaban na Amirka ke nuna take-taken nesanta kansa da kungiyar tsaro ta NATO da suke kawance tare ta fiskar samar da tsaro.