1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gambiya ta dakile yunkurin juyin mulki

December 21, 2022

Gambiya ta ce ta dakile wani yunkuri na juyin mulki, kana ta cafke sojoji hudu da ake zargin na da hannu a yunkurin hambarar da gwamnatin shugaba Adama Barrow.

https://p.dw.com/p/4LIFY
Shugaban kasar Gambiya Adama Barrow
Hoto: Valery Sharifulin/TASS Host Photo Agency /imago images

Gwamnatin Gambiyar ta bukaci jama'a da su kwantar da hankalinsu yayin da aka samu nasarar shawo kan al'amura a babban birnin kasar Banjul. Kawo yanzu dai babu wani tabbaci kan wadanda suka shirya wannan makarkashiyar.

A cikin sanarwar da gwamnatin kasar ta fitar, ta ce sojojin da aka kama a halin yanzu na taimakawa jami'an 'yan sanda da bincike yayin da ake ci gaba da neman wasu mutum auku da ake zargin da kitsa juyin mulkin da bai samu nasara.

Ko a shekarar 2017, shugaba Barrow ya fuskanci yunkuri na juyin mulki, shekara guda bayan da ya dare madafun ikon kasar.