1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Iran: rikicin Gaza ya yadu a yankin Larabawa

November 10, 2023

Ministan harkokin wajen Iran ya ce ba makawa rikicin Isra'ila da Hamas ya yadu a yankin kasashen Larabawa duba da yadda Isara'ila ta yi watsi da kiraye-kirayen tsagaita buda wuta da ake yi mata.

https://p.dw.com/p/4Yfnc
Yaduwar rikicin Isra'ila da Hamas a yankin kasashen Larabawa
Yaduwar rikicin Isra'ila da Hamas a yankin kasashen LarabawaHoto: Mohammed Al-Masri/REUTERS

A yayin wata hira ta wayar tarho jami'in diflomasiyyan na Teheran Hossein Amir-Abdollahian ya shaida wa takwaransa na Qatar Mohammed ben Abdelrahmane Al-Thani cewa la'akari da yadda yakin ke ci gaba da haddasa asarar rayukan fararen hula mazauna Gaza ya zama wajibi rikicin ya fadada a fadin yankin.

Karin bayani:  Shugaban Amurka Joe Biden ya ce babu yiwuwar tsagaita wuta a Gaza.Biden

Akalla mutane 1,400 ne suka halaka a Isra'ila tun bayan da kungiyar Hamas mai iko da zirin Gaza ta kai harin ba zata wanda ba a taba ganin irinsa ba, yayin da a bangaren Falasdinu aka sanar da mutuwar fararen hula akalla 10,812 ciki har da kananan yara 4,412.

Karin Bayani:  Turkiyya ta bukaci Amurka ta sa baki don tsagaita wuta a Gaza

To sai dai yayin da ake wannan fargaba Amurka da ke zama babbar kawar Isra'ila ta aike da jiragen yaki i zuwa Gabashin Tekun Mediteranean da nufin bai wa Isra'ila kariya da kuma dakatar da duk wani yunkuri na fadadar rikicin.