1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ISWAP ta kashe mutane a Chibok

May 4, 2022

'Yan bindigar kungiyar ISWAP, sun kai wani sabon hari a kauyen Chibok da ke arewacin Najeriya inda suka kashe mutane da kona gidaje da ma kwashe kayan abinci da farfasa shaguna.

https://p.dw.com/p/4Aowa
Karte Nigeria Borno Chibok

Rahotannin da ke fitowa daga yankin arewa maso gabashin Najeriya, sun tabbatar da wani sabon hari da mayakan tarzomar ISWAP suka kai wani kauyen Chibok da ke cikin jihar Borno.

Bayanai sun ce akalla mutum tara ne suka salwanta a harin da aka kai kauyen Kautikeri da yammacin jiya Talata, daidai lokacin da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ke ziyara a jihar.

Shaidu sun ce maharan da suka shiga cikin motoci wasu bisa babura, sun kuma kwashe kayan abinci da na shaguna a suka samu a kauyen.

Sojojin Najeriya dai ba su bayar da tabbacin faruwar harin a lokacin da ya faru ba, sai dai dagacin kauyen, Ayuba Alamson ya tabbatar da faruwar lamarin.