1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Faransa ta yi watsi da korar jakadanta

August 26, 2023

Faransa ta yi watsi da bukatar sabbin jagororin sojan Nijar, kan wa'adin sa'o'i 48 da suka ba wa jakadanta Sylvain Itte na ya tattara komatsansa ya fice daga kasar.

https://p.dw.com/p/4VbS6
Zanga-zangar adawa da Faransa a Nijar
Faransa ta yi watsi da matakin korar jakadanta Sylvain Itte daga Nijar.Hoto: Mahamadou Hamidou/REUTERS

Fadar gwamnatin Faransa (Quai d'Orsay) da kanta ce ta yi wannan martani da Yammacin Jumma'a (25.08.2023) jim bayan sanarwar majalisar sojin ta Nijar, inda ta ce sojojin ba su da hurumin daukar wannan mataki domin su ba halastatun jagorori ba ne.

Majalisar sojojin ta Nijar karkashin Birgediya janar Abdourahamnane Tiani ta ce ta dauki matakin korar jadadan na Faransa ne sakamakon kin amsa gayyata i zuwa taro da ministan harkokin kasashen ketare na Nijar din ya yi masa.

Karin bayani: Sabuwar baraka tsakanin Nijar da Faransa

Wannan takun saka da ke dada kamari tsakanin sabin jagorin sojan na Nijar da Faransa da ta yi wa kasar mulki mallaka na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyar ECOWAS ke kara matsa lamba ga sojojin na su dawo da mulkin farar hula wanda suka kifar yau da kusan wata guda yayin da sojojin ke ci gaba da sukuwa a kan dokin na ki.

Karin bayani: ECOWAS na kan bakanta a kan Nijar