1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalar musguna wa 'yan jarida na karuwa

Ramatu Garba Baba
December 9, 2021

Wani sabon rahoton kwamitin kare hakkin 'yan jarida ne ya gano karuwar matsalar musguna wa 'yan jarida da ake yi wanda ya zarta yadda al'amarin ya ke a bara.

https://p.dw.com/p/441oI
Social Card One Free Press Coalition

Kwamitin kare hakkin 'yan jarida na(CPJ) ya sheda halin tasku da 'yan jarida da dama ke ciki a sassan duniya, a rahoton kwamitin na wannan Alhamis, ya ce,  alkaluman yawan 'yan jarida da ake tsare da su a gidajen yari saboda kawai suna gudanar da ayyukansu ya haura sosai inda aka samu karin da ya zarta kima a cikin wannan shekarar ta 2021 mai karewa. 


Kididdiga na shekara-shekara na CPJ ya hada dana 'yan jarida da aka daure ko aka kashe su a sassan duniya. Daga bara ya zuwa yanzu, akalla 'yan jarida 280 ne suka samu kansu a gidan kurkuku a yayin da kimanin 'yan jarida 24 ne suka mutu a bakin aiki. Kasar Chaina ce a sahun gaba daga cikin kasashen duniya da aka fi musgunawa dama daure 'yan jarida.