1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Shugaba Ruto ya nemi a kawo karshen yakin Ukraine

Suleiman Babayo RGB
March 30, 2023

Shugaba William Ruto ya yi kira ga gwamnatin Chaina da ta yi amfani da dangartakarta da Rasha a shawarta Putin kan ya dakatar da mamayar Ukraine.

https://p.dw.com/p/4PRox
Shugaba William Ruto na Kenya
Shugaba William Ruto na KenyaHoto: DW

Shugaba William Ruto na kasar Kenya yana wata ziyara a birnin Berlin fadar gwamnatin Jamus, ziyarar na zuwa a daidai lokacin da ake samun zanga-zangar tsadar rayuwa a kasar Kenya. Shi dai Shugaba Ruto mai shekaru 56 da haihuwa wanda ya dauki madafun ikon kasar ta Kenya a shekarar da ta gabata, ya yi wata fira da DW in da ya yi bayanai kan kan mahimamcin wannan ziyara a birnin Berlin na Jamus.

Shugaban kasar ta Kenya ya nemi ganin sasantawa game da rikicin Ukraine sakamakon kutsen Rasha, abin da zai kawo karshen yuwuwar wani munmunan yaki tsakanin kasashe duniya, inda ya nuna fata kan Chaina za ta taka rawa wajen warware rikicin. Lamarin da ya shafi tsadar rayuwa musamman a kasashe masu tasowa.

Shugaban kasar Jamus Walter Steinmeier da takwaransa William Ruto na Kenya
Shugaban kasar Jamus Walter Steinmeier da takwaransa William Ruto na KenyaHoto: Annegret Hilse/REUTERS

Kan halin da kasarsa ke ciki na zanga-zanga kan matsalar tsadar rayuwa kuwa, Shugaba Ruto ya yi fatalin da batun yana mai cewa, wannan zanga-zangar siyasa kan lashe zaben shugaban kasa da ya yi na shekarar da ta gabata ne, kuma akwai 'yan adawa da ke ci gaba da yi masa irin wannan yankan bayan.

Lokacin zaben na Kenya an yi fafatawa mai zafi tsakanin jagoran 'yan adawa Raila Odinga da kuma William Ruto wanda ya yi nasara. Odinga ya zargi mataimakin shugaban kasar ta Kenya na yanzu Rigathi Gachagua da amfani da jami'an tsaro domin tozarta magoya bayan 'yan adawa, wadanda suka yi zanga-zanga kan nuna takaici da tsadar rayuwa da ake fuskanta.