1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

ISWAP ta kashe jami'an tsaron Najeriya

November 30, 2023

Mayakan kungiyar ISWAP sun kai hari da ya kashe jami'an tsaron Najeriya, kasar da ke fama da matsaloli ciki har da rashin tsaro, gagarumin aiki da ke gaban gwamnati.

https://p.dw.com/p/4ZdFQ
Motar mayakan kungiyar Boko Haram
Motar mayakan kungiyar Boko HaramHoto: Audu Ali Marte/AFP/Getty Images

Wani harin kwanton bauna da ake zargin na mayaka masu ikirarin jihadi ne, ya yi sanadin salwantar jami'an tsaron Najeriya akalla hudu a jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

Mayakan na tarzoma da ke da alaka da kungiyar IS, sun bude wuta ne a kan ayarin sojoji hadi da wasu 'yan sa-kai da ke kan hanyarsu ta komawa garin Mongono, mai tazarar mil 87 da Maiduguri babban birnin jihar ta Borno.

Hare-hare na mayakan da ke ikirarin jihadin dai sun kashe dubban mutane yayin da wasu miliyoyi suka rasa sukuni tun bayan bullar matsalar a shekara ta 2009.

Matsalar tsaro dai gagarumar matsala ce daga cikin kalubalan da gwamnatin Bola Tinubu da ta kama aiki cikin watan Mayun bana ke fuskanta a Najeriyar.